✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rasha 2018: Gwamnatin Tarayya ta ware wa Super Eagles Naira Biliyan 3

Gwamnatin Tarayya ta kudurta aniyar kashewa kungiyar kwallon kafa ta Super Eagles zunzurutun Naira Biliyan 3 a gasar cin kofin duniya da za a yi…

Gwamnatin Tarayya ta kudurta aniyar kashewa kungiyar kwallon kafa ta Super Eagles zunzurutun Naira Biliyan 3 a gasar cin kofin duniya da za a yi a Rasha a badi idan Allah Ya kaimu.

Ministan Matasa da Wasanni Mista Solomn Dalung ne ya bayyana haka ga menama labarai a ranar Talatar da ta wuce a fadar gwamnati da ke Abuja.

Ya ce za a yi amfani da  kudin ne wajen biyan ’yan kwallon alawus-alawus da ba su horo da kama musu masauki da sauran bukatunsu na yau da kullum.

Ministan ya ce Ma’aikatar matasa da wasanni ta kammala shirye-shiryen aika wata tawaga ta musamman da za ta goya wa Super Eagles baya a yayin gasar a Rasha don karfafawa ’yan kwallon gwiwa.

“Mun yanke shawarar a watan Maris na badi za mu biya dukkan alawus-alawus din ’yan kwallon don karfafa musu gwiwar tunkakar gasar, ba kamar yadda aka rika samun matsala a irin haka a baya ba”, in ji shi.

Super Eagles dai za ta fafata ne a rukunin D da kasashen Ajantina da Kuroshiya da kuma Iceland a yayin gasar.  Sau hudu kenan Eagles take halartar gasar cin kofin duniya.  Na farko shi ne a shekarar 1994 sai a 1998 sai a 2002 sai kuma yanzu a 2018.