✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NFF ta ƙaryata dakatar da Osimhen

Har ya zuwa yanzu babu wata sanarwa a hukumance da take nuna dakatar da ɗan wasan

Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF) ta ƙaryata dakatar da ɗan wasan tawagar Super Eagles, Victor Osimhen.

Hukumar ta ce, labarin kanzon kurege ne kawai wasu daga cikin jaridu na intanet ke yaɗawa game da dakatar da ɗan wasan.

Jaridu da dama sun wallafa cewa NFF ta sha alwashin hukunta Victor Osimhen ne har sai ya bayar da haƙuri kan wani bidiyo da ya wallafa na caccakar tsohon kocin Najeriya Finidi George da ya ajiye aiki a bayan nan.

Babban Sakataren Hukumar, Dakta Mohammed Sanusi, ya bayyana mamakinsa da ganin yadda labarin ya yadu a wasu kafafen watsa labarai, inda ya ce har ya zuwa yanzu Hukumar ba ta kammala yanke hukunci kan dan wasan ba.

“Har ya zuwa yanzu babu wata sanarwa a hukumance da take nuna dakatar da ɗan wasan.

“Abin da muka fi mayar da hankali a kai yanzu shi ne mu ga mun shawo kan matsalolin da suka dabaibaye tawagar ta Super Eagles,” in ji sanarwar.