✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Najeriya ta ƙara kuɗin yin takardar fasfo

An ƙara kuɗin mallakar fasfon ne a gida Najeriya kaɗai, bai shafi masu yi a kasashen waje ba

Gwamnatin Najeriya ta sanar da kara kuɗin mallakar takardar fasfo tafiye-tafiye da kashi 43%.

Hukumar Shige da Fice ta bayyana cewa an ƙara kuɗin mallakar fasfon a gida Najeriya ne kawai, bai shafi masu yi a kasashen waje ba.

Sanarwar da kakakin hukumar, Kenneth Udo, ya fitar ta ce takardar fasfo mai shafi 64 ya tashi daga N75,000 ya koma N100,000.

Fasfo mai shafuka 32 kuma an ƙara kudin mallakarsa daga Naira dubu 35 zuwa Naira dubu 50.

Sanarwar ta ranar Laraba ta ce sabon farashin zai fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Satumba, 2024.

A cewarsa, an ƙara kuɗin mallakar fasfo ɗin ne da sun kara ingancinsa da nagaratarsa.