Gwamnatin tarayyar Najeriya ta sanar da ranakun 25 ga watan Disamba da 26 wato Laraba da Alhamis da kuma 1 ga Janairun 2020 a matsayin hutun Kirsimati da kuma na sabuwar shekara.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da Barista Georgina Ehuriah ya fitar a madadin gwamnatin tarayya.
Sanarwar ta kara da cewa, Ministan ya taya Kiristoci da kuma ‘yan Najeriya murna da kuma yin kira da zauna lafiya yayin bukukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara.