Qungiyar Super Eagles ta Njeriya da Aljeriya sun tashi kunnen doki a birnin Constantine.
Wannan wasan yana cikin wasannin neman gurbi a gasar cin kofin duniya da zai wakana badi a qasar Rasha.
Wannan sakamakon bai da wani illa ga Najeriya, domin ta riga ta samu gurbi a gasar,
Dan wasan Najeriya John Ogu ne ya fara zura kwallo a ragar Aljeriya a minti na 63, sannan sai kyafin din Aljeriya ya farke musu, inda ya zura bugun daga kai sai gola daga baya,