✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum 6 sun mutu sakamakon hatsarin mota a Zamfara 

Hatsarin ya auku ne sakamakon gyaran tituna da ake yi a jihar.

Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) a Jihar Zamfara ta tabbatar da mutuwar mutum shida a Gusau, sakamakon wani hatsarin mota.

Kwamandan hukumar a jihar, Iro Danladi, ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) a Gusau a ranar Talata.

Ya bayyana cewa ya kamata a wayar da kan mutane game da gyaran tituna da ake yi a jihar.

Wadanda abin ya shafa galibin mata ne da yara kanana da ke tsallaka titi.

Danladi ya gargadi direbobi da su yi taka-tsan-tsan tare da rage gudu don guje wa yanayin da ba a shirya masa ba.

A cewarsa, duk da cewa ma’aikatan hukumar suna kan hanyoyin don saukaka zirga-zirga, amma akwai bukatar kamfanonin gine-ginen da ke gudanar da ayyukan tituna a jihar su samar da isassun alamun hanyoyin don jan hankalin masu ababen hawa da jama’a.

Ya yi kira ga gwamnati da ta fadakar da jama’a kan yadda za a yi amfani da hanyoyi a wannan lokaci na ayyukan gyaran tituna, la’akari da sauye-sauyen tsarin zirga-zirga.

Danladi ya ce ya kamata gwamnati ta dauki nauyin wayar da kan jama’a a kafafen yada labarai game da hanyoyin da ake gyara don kauce wa rasa rayuka da dukiyoyi.