✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum 3 sun mutu yayin da tanka ta murƙushe adaidaita sahu a Jos

FRSC ta tabbatar da faruwar lamarin a daren ranar Litinin.

Mutum uku sun rasa rayukansu, yayin da wasu huɗu suka jikkata, bayan da wata tankar mai ta muƙushe adaidaita sahu a Jihar Filato.

Hatsarin ya faru ne a kan titin Farin Gada da ke Jos ta Arewa, kusa da Gidan ɗaliban Jami’ar Jos.

Kakakin Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC) a jihar, Peter Yakubu, da Sakataren Ƙungiyar Agaji ta Red Cross, Nura Ussaini Magaji, sun tabbatar da faruwar lamarin.

Sun ce wasu daga cikin waɗanda suka rasa rayukansu sun yi raga-raga ta yadda ba a iya gane su.

“Abubuwa biyu ne suka yi taho-mu-gama – wata tankar mai da adaidaita sahu.

“Mutum uku sun mutu, sannan mutum huɗu sun samu raunuka a hatsarin,” in ji Yakubu.