✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151

Mutane 3,018 sun rasa matsugunansu a sakamakon ambaliyar da ta shanye al’ummomi uku

Adadin mutanen da suka mutu a mummunar ibtila’in ambaliya a Jihar Neja ya karu zuwa mutum 151.

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ce ta sanar cewa mutane 11 sun jikkata, yayin da mutane 3,018 suka rasa matsuguninsu a ibtila’in na ƙaramar hukumar Mokwa a safiyar Asabar.

Kakakin hukumar, Ibrahim Hussaini, ya bayyana cewa ambaliyar ta shafi gidaje 265 da kuma magidanta 503.

Ya ƙara da cewa yankuna uku, da suka hada da Tiffin Maza da Anguwan Hausawa, sun nutse sakamakon ruwan sama mai ƙarfi da aka yi na tsawon sa’o’i da dare a ranar Laraba.

Wannan lamari ya faru ne watanni biyar bayan Gwamnan Jihar Neja, Umar Bago, ya sanar da cewa jihar ta samu tallafin dala miliyan 10 daga Bankin Duniya don dakile zaizayar ƙasa a wasu sassan Mokwa.

Gwamnan ya ce an tantance kwararrun ’yan kwangila don gudanar da aikin.

A ranar Juma’a, Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a yayin miƙa ta’aziyyarsa, ya umarci Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da hukumomin tsaro su ƙara ƙaimi wajen aikin ceto da agaji a wuraren da abin ya shafa.