✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mu rika kula da mutuncin kanmu 1

A wannan mako mun dauko wani rubutu ne daga Kundin Solana Olumhense da jaridarmu ta Ingilishi Sunday Trust ta farkon wannan mako ta buga, inda…

A wannan mako mun dauko wani rubutu ne daga Kundin Solana Olumhense da jaridarmu ta Ingilishi Sunday Trust ta farkon wannan mako ta buga, inda ya yi sharhi kan korar ministoci tara da Shugaba Jonathan ya yi a makon jiya. Marubucin ya tabo batun jami’an gwamnati su koyi dabi’ar tsira da mutuncinsu tun kafin a zubar musu da shi a kasuwa:
A makon jiya ne aka kori ministocin Najeriya tara wadanda rikicin shugabancin da ke addabar jam’iyya mai mulki PDP ya jawo musu haka. Abin takaici an sallami ministocin ne ba domin a inganta majalisar zartarwar ba. Da saboda haka ne ministoci da dama za a sallama.
Abin da girgizawa ganin yadda aka tozarta Ministan Tsare-Tsaren kasa Shamsudeen Usman. A wani rubutu da na yi a watan Maris din 2012, na nemi kada ya jira sai an sallame shi, saboda gwamnatinsa ta yi karya game da shirinta na sake fasalin kasa da Ministan ya shaida wa ’yan Najeriya su sa rai a kai a watan Oktoban 2011.
Malam Usman ya ce shirin zai magance matsalolin rashin da’a da ke addabar kasar nan. Ya shaida wa manema labarai cewa: “A cikin dukkan al’ummu, idan ba ka da tsarin da ke kamawa ya hukunta wadanda suke saar dukiyar jama’a, to za su ci gaba da yin satar.  Wadannan suna daga cikin abubuwan da shirin sake fasalin kasa zai magance… Wajibi ne mu karfafa bin doka da inganta bangaren shari’a da aikin dan sanda. Idan ka san akwai dama kashi 99 cikin 100 na a kama ka idan ka yi sata, kuma akwai kashi 100 na tabbacin za ka tafi kurkuku, ba za ka yi satar ba.”
Sai dai wannan ba gaskiya ba ne. Wannan shiri da ake kira na sake fasalin kasa ya saba kwata-kwata da wannan yunkuri na magance wadannan matsaloli. Ya bayyana a fili cewa wani mamunga ne aka shirya domin yaudarar talakawa da masu rauni.
Abin da yake fili shi ne zamanin “Shirin Sake Fasalin,” sabanin yyadda tsohon Ministan ya nuna, baun bin doka da oda ya zama abin ba’a. Saboda idan muka leka wani gefen za mu ga idan ka yi babbar sata, akwai tabbaci 100 bisa 100 za a ba ka lambar yabo ta kasa, ba daurin da za a I maka kamar yadda lamarin Dipreye Alamieyeseigha ya nuna. Shirin Sake Fasalin kasar ya tabbata gangariyar 419: ga dadin fada, amma idan ka kale shi labarin kanzon kurege ne.
Wannan ne ya san a I faa Usman, a matsayinsa na dalibin mashahuriyar jami’ar nan ta Ahmadu Bello da Makarantar Tattalin Arziki da Kimiyyar Siyasa ta Landan, zai gane ya saba alkawarinsa ya sauka daga mukaminsa.
Amma bai gane ba, balle ya sauka. Haka wannan tabargaza ke ci gaba, wasu manyan jami’an gwamnati suna ta sakin baki suna lullube gaskiyar lamari kan wannan shiri na yaudara. Ta hanyar ci gaba da zama a gwamnati, Usman ya taimaka a cimma nasarar wannan munfunci, koda kuwa bai taimaka wajen shirya shi ba. Sai ga shi a makon jiya kwadayinsa ya jawo masa tozarta, kuma ina fata zai dauki lokaci yana auna irin kason yaudarar da jami’an gwamnati ke yi.
Wannan shi ne irin yanayin rayuwar mutane a Najeriya: wato rashin tsare mutunci. Kamar yadda na fada kan ministoci a lokacin, “daki ne mai munin shiga a lokacin da kowa ya san hakikanin yadda matsala take, kuma babu wanda yake da azamar gyara a kai. Wannan daki gidan wuta ne ba Tudun La’arafi.”
Baa bin mamaki ba ne da jirin ministocin da aka sallama bai kunshi na Ministan Man Fetur ba Misis
Diezani Allison-Maduekwe. Kuma bai kunshe da sunan Babban Lauyan Najeriya kuma Ministan Shari’a Mohammed Adoke Bello ba.  
Idan aka zo batun almundahana, ko shakka babu Allison-Madueke ce minister da ta fi fice a duniya. Kusan a kowane wata sai an yi zargin samun hannunta a keta wata doka ko ka’ida. Zargi ba daidai da tabbatar da laifi ba ne, amma kuma ba ya nufin mutumin na da gaskiya, wata hujjar da gwamnati mai amana ya kamata ta kula da ita. Kuma duk da haka, ko sau daya Gwamnatin Tarayya ba ta taba bincikar wani zargi da aka yi mata ba, ko don ta kunyata masu zargin ko ta tabbatar da gaskiyar Ministar. Sannan ko sau daya Ministar a kashin kanta ba ta taba mika takardar murabus ba, ko ta nuna wata damuwa kan mutuncinta.  
Haka lamarin yake ga Minista Bello, wanda ba ma an zarge shi da azurta kansa ta haram ba ne kawai, har da yadda yake tankwara Ma’aikatar Shari’a wajen aikata zalunci da barna. Nan ma gwamnati ko Minista Bello sun ki nuna cewa akwai babbar matsala lokacin da aka zargi babban lauyan gwamnatin da rashin da’a da aikata mugun laifi.