✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Masu yada labaran karya a Intanet za su gamu da azabar Allah – Umar Sani Fagge

Ya ce azabar na jiran duk wanda ya mutu yana aikata laifin bai tuba ba

Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan da ke jihar Kano, Sheikh Umar Sani Fagge, ya ce akwai azabar da ke jiran masu kirkirar karya da yadata a shafukan sada zumunta na intanet.

Shehun malamin, wanda kuma Farfesan Larabci ne a Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK), ya yi wannan gargadi ne a wata lakca da ya gabata kan kafar sadarwa ta intanet, da dandalin sada zumunta da muhawara, da kuma yadda matasa ke amfani da su a yanzu.

Ya bayyana irin narko da azabar da aka tanadar wa mai dabi’ar a lahira matukar ya mutu bai tuba ba.

“Za kwantar da mutum a rika yi masa zane a fuskarsa da faratan wuta, tun daga bakin gashinsa har zuwa karshen kuncinsa.

“Ana gamawa sai a juya daya kan kuncin nasa a sake nutsa wadannan farata na wuta, a zane ta kamar yadda aka yi waccan. Kafin a gama waccan da aka yi ya warke, sai a juya fuskar a maimaita,” inji malamin.

Ya ce haka za a yi ta yi wa mutum a wutar jahannama babu ranar da za a daina.

Daga karshe ya yi kira ga matasa da su san irin labaran da za su rika yadawa a intanet don guje wa fadawa cikin fushi da kuma azabar Allah idan sun mutu.

Wannan gargadi ya zo ne a daidai lokacin da ake kirkirar labaran karya a yada a intanet don jan hankalin masu amfani da shafukan na sada zumunta.