✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Masu cutar coronavirus a Najeriya sun doshi 5,000

A Najeriya, an samu karin mutane 242 da aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19 a sa’o’i 24. Alkaluman baya-bayan nan da Hukumar Yaki da…

A Najeriya, an samu karin mutane 242 da aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19 a sa’o’i 24.

Alkaluman baya-bayan nan da Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta fitar sun nuna cewa hakan ya kawo jimillar wadanda suka kamu a kasar zuwa 4,641.

Hukumar ta ce a daren 10 ga watan Afrilu ta bada bayanan da suke ba daidai ba na adadin wadanda suka mutu a sakamakon cutar a jihar Nasarawa, inda ta nemi afuwa daga ‘yan Najeriya.

“Mutum daya aka rasa a jihar Nasarawa, ba biyu ba kamar yadda muka fada a baya, muna neman afuwan gwamnatin jihar tare da tabbacin bada ingantattun bayannai.

‘zuwa tsakar daren Litinin adadin wadanda aka sallama ya tashi 902‬, yayin da wadanda suka mutu suka kai 150.

Galibin sabbin majinyatan dai, wato 88, a jihar Legas suke, 64 a Kano, 49 a Katsina, 13 a Kaduna.

Sai kuma jihar Ogun mai mutum tara, shida a Gombe, hudu a Adamawa, da kuma uku   Yankin Babban Birnin Tarayya.

Yayin da jihohin Ondo‬, Oyo‬, Rivers‬, Zamfara‬, Borno‬, da Bauchi‬ ke da mutum daya daya da suka kamu.