✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mako 1 da fara yaki, ’yan Ukraine miliyan 1 sun fice daga kasar

Mako daya da fara gwabza yaki, mutum miliyan daya sun fice daga Ukraine, miliyan 12 za su rasa muhallansu

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ’yan kasar Ukraine akalla miliyan daya ne suka tsere daga kasar tun bayan da sojojin Rasha suka kutsa cikinta da yaki a makon da ya wuce.

Shugaban hukumar kula da ’yan gudun hijira ta majalisar, Filippo Grandi, ya bayyana alakaluman ne mako guda bayan barkewar yakin da Rasha ta kaddamar a Ukraine.

Grandi, wanda ya bukaci a tsagaita wuta a tashin hankalin domin tallafa wa miliyoyin jama’ar Ukraine da suke bukatar agaji a cikin kasar, ya ce suna hasashen cewa rikicin na iya raba mutane kusan miliyan 12 da muhallansu a fadin kasar.

Rusha ta bayyana aniyarta ta tattaunawar tsagaita wuta tare da Ukraine bayan da dakarunta suka kai munanan hare-hare a wasu biranen kasar, yayin da rahotanni suka ce ana fada gaba da gaba a titunan birnin Khirkov.

Ukraine ta ce tawagar wakilanta sun kama hanyar zuwa wurin tattaunawa da Rasha a kusa da iyakar kasar Poland, sai dai kuma Ministan Harkokin Wajen kasar, Dmytro Kuleba, ya ce ba za su lamunci a gindaya musu sharuda ba.

Rahotanni sun bayyana cewa daruruwan mutane sun mutu a sakamakon yakin da ake gwabzawa, yayin da dubbai ke ci gaba da tserewa suna barin kasar domin samun mafaka a wasu kasashe.