✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Majalisa ta mika wa Buhari kasafin kudin 2022

Muna sa ran kafin 31 ga watan Disamba Buhari zai sanya hannu a kan kasafin kudin.

Majalisar Dokokin Tarayya ta mika wa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari kasafin kudin kasar na badi domin ya rattaba hannu a kai.

Wata majiya daga ofishin Magatakardan Majalisar da ta tabbatar da hakan, ta ce an mika wa shugaban kasar kasafin kudin ne tun a ranar Lahadi, 26 ga watan Disamban 2021.

A cewar majiyar, ana sa ran Shugaba Buhari zai rattaba hannu kan kasafin kudin kafin ranar 31 ga watan Disamban 2021, a yayin da za a yi bankwana na karshe da shekarar.

“Muna sa ran kafin 31 ga wata, za a sanya hannu a kan kasafin kudi,” a cewar majiyar.

“Tun a ranar Lahadi, 26 ga wata aka mika wa shugaban kasa kasafin kudin.

“An aika da kasafin kudin ne a ranar 24 ga watan kuma ya zuwa 25 ga wata da ta kasance ranar Kirsimeti, kasafin kudin ya kasance tare da shugaban kasa.”

Majiyar ta kuma karyata rade-radin da suka rika yaduwa a bayan nan cewa ba a aike wa shugaban kasa kasafin kudin ba yayin da ya rage kwanaki uku a yi bankwana da shekarar 2021.

Ana iya tuna cewa, a makon jiya ne zauren Majalisun Tarayya biyu da suka hada da na Wakilai da Dattawa suka amince da kasafin kudin na badi gabanin su tafi hutunsu na karshen shekara.