Hukumar Jindadin Alhazan Najeriya ta Kasa (NAHCON) ta ce ta dawo da alhazan Najeriya dubu 40,821 gida Najeriya daga kasar Saudiyya bayan kammala aikin hajjin bana na shekarar 2019 cikin nasara.
Cibiyar hukumar NAHCON da ke birnin Makkah ce ta sanarwa Kamfanin Dillancin Labarai NAN hakan yau Litinin. Mahajjatan da suka dawo gida na karshe a yazu su ne alhazan jihar Filato 555 tare da jami’an NAHCON a jirgin saman Max Air flight NGL 2110.