Magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal sun bukaci a dawo da tsohon dan wasansu wanda ya yi ritaya daga buga wa kungiyar kwallon kafa Nwanko Kanu.
Tohon dan kwallon Najeriya, Kanu ya zura kwallaye uku ne a wani wasa da aka buga tsakanin tsofaffin ’yan kwallon Arsenal da kuma tsofaffin ’yan kwallon kulob din AC Milan na Italiya inda kungiyar Arsenal ta lashe wasan da ci 4 da 1.
Bayan wasan ne wadansu daga cikin magoya bayan kungiyar suka bukaci lallai kungiyar ta dawo da Kanu Nwanko domin ya ci gaba da buga wa kungiyar wasa. A cewarsu har yanzu akwai sauransa hasali ma ya fi da yawa daga cikin ’yan wasan da suke buga wa kungiyar wasa a yanzu.
Daga cikin wadanda suka nuna bukatar a dawo da Kanu sun hada da wani mai suna George inda ya yi rubutu a shafinsa na Twitter yana cewa: “Kanu ya tafi amma bayan shekara 14 ya dawo ya zura kwallaye uku sama da Giroud.” Giroud dai shi ne dan wasan gaba a kulob din Arsenal a halin yanzu.
Shi ma wani mai suna Anie dtian ya rubuta a shafinsa cewa “Duk da cewa Kanu ya yi ritaya, amma ya nuna ya fi Giroud hikima da kwazo, don haka ya kamata kocin Arsenal, Arsene Wenger ya dawo da shi.”
Magoya bayan Arsenal sun bukaci a dawo da Kanu
Magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal sun bukaci a dawo da tsohon dan wasansu wanda ya yi ritaya daga buga wa kungiyar kwallon kafa…