Leicester City za ta sayar da dan Najeriya Kelechi Iheanacho a watan Janairu watanni kadan bayan ta saye shi a kan kudi Fam miliyan 25 da Manchester City ko da kuwa za ta asara ne.
Rahotanni sun nuna cewa ana biyan Iheanacho albashin kudi na fam dubu 115 a mako, wanda ya kama Naira biliyan 2.9 ke nan a shekara.
Tun zuwansa kungiyar, dan shekara 21 Iheanacho ya buga wasan rukunin Firimiya sau biyu ne kawai.