A yau Laraba kotun koli ta tabbatar da nasarar zaben Gwamna Babajide Sanwo-olu a matsayin zababben Gwamnan jihar Legas.
Alkalin kotun Paul Galinje, ne ya sanar da nasarar zaben Gwamna Babajide Sanwo-olu bayan yin watsi da daukaka karar da aka shigar kotun har sau biyu. An yi watsi da karar ne bayan rashin gamsar da kotun.