Kotun daukaka kara, da ke Abuja, ta yi watsi da korafin da korarren Alkalin alkalan Najeriya Walter Onnoghen, ya shigar gabanta, inda yake kalubalantar umurnin da aka yi na ya ajiye aikinsa dole, kuma shugaba Buhari ya nada babban jojin rikon kwarya.
Da take yanke hukunci, kotun daukaka karar, ta ce aikin-gama, ya riga ya-gama, gabanin Mista Onnoghen din ya gabatar da karar tasa.