Kotun Da’ar Ma’aikata ta yanke wa tsohon Babban Jojin Najeriya mai shara’a Walter Onnoghen hukunci.
Kotun ta yanke cewa a sauke shi daga mukaminsa, sannan duk dukiyoyi da kadarorin da ake zarginsa da su a kwace a mayar asusun gwamnati, sannan kuma ta dakatar da shi daga rike mukami a Najeriya na tsawon shekara 10.