✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kofin Duniya 2026: Yadda kasashen Afirka za su fafata wajen neman tikiti

Najeriya da Afirka ta Kudu da Benin da Zimbabwe da Rwanda da Lesotho na rukuni daya.

Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka CAF a madadin FIFA ta fitar da jadawalin wasannin neman gurbi a gasar Kofin Duniya bangaren kasashen Afrika.

Jadawalin wanda CAF ta fita a ranar Alhamis a birnin Abidjan na kunshe da kasashe 54 wadanda aka rarraba rukunnai 9 da za su fafata a wasannin gida da waje don fitar da zakaru a cikinsu.

Jadawalin ya nuna cewa rukunin A na kasashen na kunshe da Masar da Burkina Faso da Guinea Bissau kana Saliyo sai Habasha sannan Djibouti.

A rukunin B akwai kasashen Senegal da jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo kana Mauritania sai Togo da Sudan da kuma Sudan ta kudu.

Bangaren rukunin C kuwa ya kunshi kasashen Najeriya da Afirka ta Kudu kana Benin da Zimbabwe sannan Rwanda da Lesotho.

Rukunin D na dauke da kasashen Kamaru da Cape Verde da Angola da Libya sannan Eswatini sai Mauritius.

Rukunin E kuwa akwai kasashen Morocco da Zambia da Congo Brazzaville da Tanzania sai Jamhuriyar Nijar kana Eritrea.

Rukunin F na kunshe da Ivory Coast da Gabon da Kenya da Gambia sannan Burundi sai tsibirin Seychelles.

A Rukunin G akwai kasashen Algeria da Guinea da Uganda da Mozambique kana Bostwana da Somalia.

Jadawalin na CAF na nuna cewa a rukunin H akwai Tunisia da Equatorial Guinea kana Namibia sannan Malawi da Liberia da kuma São Tome and Principe.

Rukunin I kuma na karshe a wannan jadawali na dauke da kasashen Mali da Ghana sannan Magadascar sai Jamhuriyyar Afirka ta Tsakiya sannan tsibirin Comoros kana Chad.