✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jirgin Max Air da ya makale da alhazai a Nijar ya samu izinin tashi

Jirgin ya tafi birnin Jidda na kasar Saudiyya domin kwaso ragowar alhazan Najeriya zuwa gida

Jirgin kamfanin MaxAir da ke jigilar alhazan Najeriya wanda ya makale a Jamhuriyar Nijar sakamkon juyin mulki ya samu izinin tashi.

Hukumar gudanarwar MaxAir ta sanar cewa tuni jirgin samfurin Boeing 747-400 ya bar kasar zuwa birnin Jidda na kasar Saudiyya domin kwaso ragowar alhazan Najeriya zuwa gida.

Kamfanin ya fitar kafin wayewar garin Juma’a, awanni bayan makalewar jirgin a kasar Nijar, yana godiya ga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki a harkar sufurin jiragen sama a Najeriya da suka sanya baki aka saki jirgin.

A ranar Alhamis MaxAir ya tabbatar da cewa jirinsa mai lamba 5N-ADM, an hana shi tashi ne bayan ya sauke rukunin karshe na alhazan Nijar, a ranar da sojojin kasar suka yi wa Shugaba Mohamed Bazoum juyin mulki.

MaxAir na daga cikin kamfanonin jiragen sama na cikin gida a Najeriya da Hukumar Aikin Hajji ta Kasa ta ba wa aikin jigilar alhazai a bana.

Kamfanin wanda mallakin attajiri dan asalin jihar Katsina, Alhaji Dahiru Mangal ne, ya jima yana wannan aiki.