✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jinjina ga ‘yan Najeriya kan zaben da suka yi cikin lumana

Nura Sani Rijau Assalamu alaikum Editan  jaridar Aminiya mai tarin albarka. Ina  so ku ba ni dama in yi  yabo da jinjina  ga ’yan uwana…

Nura Sani Rijau

Assalamu alaikum Editan  jaridar Aminiya mai tarin albarka. Ina  so ku ba ni dama in yi  yabo da jinjina  ga ’yan uwana ’yan Najeriya bisa zaben da suka fito kwansu da kwarkwata suka yi cikin ruwan sanyi da lumana.

Babu shakka yanzu kan ’yan Najeriya ya fara wayewa, lura da yadda zaben bana ya bambanta da na shekarun da suka shude, inda  za ku ga matasa  kai har ma da kananan yara wadansu ’yan siyasa  marasa kishin kasa na sayen kayan  maye  da gusar da hankali suna ba su, sannan su sayi makamai  su raba musu a lokacin zabe don su je su tayar da hankali. Wani lokaci su tayar da kayar baya a  inda ba a yi musu yadda suke so ba su sara ko su kashe  wanda suka so. To alhamdulillahi wannan zaben Allah Subhanahu Wata’ala Ya kawar mana da wannan muguwar dabi’a musamman jihohin da aka zaci  faruwarsa sai ga shi Allah Ya kare!

A mafi yawan jihohin Najeriya, musamman Arewa ban ji inda aka ce an yi rikici ko tayar da hankali wurin zabe ba, wannan abin alfahari ne da jin dadi ga duk mai kishin kasarmu Najeriya,

Da haka ne kuma nake amfani da wannan dama wajen kara kira ga ’yan kasa musamman matasa da yara cewa a zaben gwamnoni da na na majalisun jihohi da za a yi a mako mai zuwa su natsu su fito kwansu da kwarkwata su yi zabe cikin lumana da kwanciyar hankali, ba hayaniya ba fada kamar yadda suka yi a na Shugaban Kasa da sanatoci da  ’yan Majalisar Wakilai.

Ya kamata fa mu lura da wani abu, wadannan ’yan siyasar da ke bai wa matasa kwayoyi da makamai suna bangar siyasa wallahi tallahi ba sa bari ’ya’yansu su fito a yi da su. Ku yi dubi ku gani mana, kun taba ganin dan siyasa a shiyyarku da ’ya’yansa suka fito banga, bayan sun sha  kwayoyin maye? Da haka ne za ku  gane  cewa duk wani dan siyasa ’ya’yansa na birni suna hutawa, idan lokacin saka su makaranta ya yi za su dauke su saka su a manyan makarantu masu tsada su yi karatu, Idan sun kammala karatun kuma za ku ga sun dauke su sun kai su manyan  ofisoshin gwamnati suna aiki, mu ko ’ya’yan talakawa muna nan kawai kara zube muna biye da su, shin ba za mu yi hankali ba ?

A karshe ina rokon Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya zaba mana shugabanni nagari kuma nagartattu masu kishin kasa da al’ummomin  da suke shugabanta ba masu kishin aljifansu ba amin.

Daga Nura Sani Rijau

08108291641/ 08026664213.