✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jamilu Collins zai yi jinya zuwa karshen kakar wasanni ta bana

Jamilu ya buga wa Najeriya kwallo a gasar Cin Kofin Afirka a watan Janairu.

Dan wasan baya na tawagar Najeriya da kungiyar kwallon kafa ta Cardiff City, Jamilu Collins, zai yi doguwar jinya sakamakon rauni da ya samu a gwiwa.

Jamilu wanda rahotanni ke cewa ya kara wa Cardiff City farin jini, ya gurde ne a gwiwa a karawarsu da West Bromwich Albion wanda aka tashi canjaras babu ci.

Ana sa ran za a yi wa Jamilu aiki a gwiwar tasa cikin ‘yan makonnin masu zuwa, wanda zai shafe tsawon lokaci yana jinya har zuwa kakan wasanni ta badi mai zuwa.

Tuni abokan wasansa a kungiyar ta Cardiff suka soma kewarsa, inda kocin kungiyar, Steve Morrison ke tausaya wa dan wasan laakari da cewa ba zai sake taka leda ba sai a kaka wasanni mai zuwa.

Morrison ya kuma yaba wa kwazon Jamilu, wanda aka bayyana a matsayin dan wasan baya mafi kwarewa a gasar Ingila ajin ’yan dagaji wato Championship.

Ana iya tuna cewa, Morrison ne ya dauko Jamilu daga kungiyar 3 Liga mai buga gasar Bundesliga aji ’yan dagaji na uku a lokacin bazarar da ta wuce.

Kafin nan, Jamilu ya buga wa Najeriya kwallo a gasar Cin Kofin Afirka a watan Janairu tare da Alex Iwobi da kuma Kelechi Iheanacho.