✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

AFCON 2024: Za mu dau fansa a kan Guinea Bissau — Iwobi

Super Eagles ta koma ta biyu a teburin neman cancantar zuwa AFCON 2024.

Dan wasan Everton da Najeriya, Alex Iwobi ya sha alwashin cewa tawagar Najeriya ta Super Eagles za ta dauki fansa kan rashin nasarar da ta yi 1-0 a gida a hannun Guinea Bissau a wasan neman tikitin shiga Gasar Kofin Afirka a ranar Juma’a.

Dan wasan Guinea Bissau, Mama Balde ne ya ci wa tawagar kasarsa kwallo daya tilo ta wasan, kwallon da ta makale kenan har sai da aka tashi.

Iwobi, wanda ke wasa a gasar Firimiyar Ingila ya ce ya zama wajibi su mayar da martini dangane da wannan ci da Guinea Bissau ta yi musu.

Ya sha alwashin cewa za su kara azama a haduwarsu ta biyu, yana mai neman goyon bayan magoya bayan tawagar ta Super Eagles don cimma haka.

Da wannan sakamakon Guinea Bissau ta koma ta daya a rukunin farko da maki bakwai, bayan da ta ci Super Eagles da cin Sao Tome da canjaras da Saliyo.

Super Eagles ta koma ta biyu da maki shida, bayan nasara a kan Saliyo da Sao Tome.

An dai yi wasa na uku-uku a rukunin farko don neman gurbin shiga babbar gasar kwallon kafa ta Afirka da za a yi a Ivory Coast a 2024.

Ranar Laraba Saliyo da Sao Tome suka tashi wasa 2-2 a daya karawa ta uku a rukunin farko.

Ranar Litinin 27 ga watan Maris Super Eagles za ta ziyarci Guinea Bissau, domin buga wasa na hur-hudu a rukunin farko.

Ita kuwa Sao Tome za ta karbi bakuncin Saliyo ranar Lahadi 26 ga watan Maris.

Guinea-Bissau na da maki 7, Najeriya 6, Sierra Leone 2 kana Sao Tome da Principe na da maki 1 a teburin wannan fafutukar neman cancantar zuwa AFCON ta 2024.