✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ivory Coast ta lashe gasar AFCON ta 2023

Ivory Coast ta zama zakara bayan doke Najeriya.

Kasar Ivory Coast ta lashe Gasar Cin Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) na 2023, bayan doke Najeriya da ci 2 da 1 a wasan karshe na gasar.

Mai masaukin bakin ta zama zakara ne, bayan ta warware kwallon da Najeriya ta jefa mata kafin tafiya hutun rabin lokaci.

Dan wasan bayan Najeriya, Troost Ekoong ne ya fara jefa mata kwallo a minti na 38.

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Ivory Coast ta warware kwallon a minti na 62 daga hannun dan wasan tsakiyarta, Franck Kessie.

A minti na 81 Sebastian Haller ya kara wa mai masaukin baki kwallo ta biyu a raga, wanda hakan ya sanya ta zama zakarar AFCON ta 2023.

Idan ba a manta ba Najeriya ta doke Ivory Coast a wasan rukuni da suka fafata da ci daya ta hannun Troost Ekoong a bugun fanareti.