Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ta hanyar rataya ga mutumin da aka kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri.
Mahukunta a bangaren shari’ar sun ce an kama Esmail Fekri a shekarar 2023 yana ƙoƙarin miƙa wa Isra’ila bayanan sirri ne don samun kuɗi.
- KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna
- Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
Wannan ne karo na uku a baya-baya nan da Iran ke aiwatar da hukuncin kisa saboda zargin leƙen asiri ga Isra’ila.
A ranar Lahadi, Isra’ila ta ce ta kama wasu ’yan ƙasa biyu da ake zargin suna aiki da hukumar leƙen asirin Iran.
Babban alƙalin Iran, Gholamhossein Mohseni Ejei, ya bayyana a ranar Litinin cewa, la’akari da yanayin “yaƙi” da suke ciki, dole ne a gudanar da shari’o’i ga waɗanda ake zargin suna aiki da Isra’ila cikin hanzari.
Bayan shafe gomman shekaru ana sa-in-sa tare da nuna wa juna yatsa, a ranar Juma’ar da ta gabata Israila ta kaddamar da wani farmaki na ba-zata wanda ta ce tana kai hari kan makaman nukiliyarta.
Kawo yanzu dai rayukan mutane 224 sun salwanta a kasar ciki har da manyan dakarun sojoji, kwararrun manazarta kimiyyar makaman nukiliya da kuma fararen hula.
Sai dai tuni ita ma Iran din ta mayar da martani tana mai luguden wuta ba dare ba rana a kan Isra’ila da zuwa alkaluman da ofishin firaiministan kasar ya fitar sun ce rayukan mutane akalla 24 sun salwanta.