✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hukumar tace fina-finai ta soke lasisin gidajen gala 8 a Kano

Hukumar ta ce ta kama gidajen galar da saɓa wasu dokokinta.

Hukumar Tace Fina-finai da Ɗab’i ta Jihar Kano, ta soke lasisin gidajen wasannin gala guda takwas bisa karya wasu dokokinta.

Idan za a tuna a kwanakin baya hukumar, ta soke lasisin wasu gidajen galar bisa samun su da laifin karya dokar hukumar.

Cikin sanarwar da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya fitar, ya zayyano wuraren da hakan ta shafa da suka haɗa da Hamdala Entertainment, Lady J Entertainment, Ɗan Hausa Entertainment da Ni’ima.

Sauran sun haɗa da Babangida Entertainment, Harsashi Entertainment, da kuma Wazobiya.

Idan ba a manta ba hukumar a baya-bayan nan ta dakatar da haska wasu fina-finai 22 da suka haɗa da Dadin Kowa, Labarina, Garwashi, Gidan Sarauta da wasu.

Amma bayan wani taron masu ruwa da tsaki na Kannywood an bai wa masu shirya fina-finan wa’adin mako guda don tantance su.

A ranar Talata ma hukumar ta dakatar da yin tallan magungunan gargajiya a cikin fina-finai ko a kan titin har sai an tantance su.