✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnatin Sojin Nijar ta yi wa ECOWAS martani

Gwamnatin Sojin Nijar ta yi wa ECOWAS raddi kan wa'adin mayar da Bazoum kan mulki da ta bayar.

Gwamnatin Sojin Nijar ta gargadi Kungiyar Kasashen Yammacin Afirka ta ECOWAS a kan kada ta kuskura ta tura dakaru Jamhuriyar Nijar.

Janar Abdourahmane Tchiani wanda ya ayyana kansa a matsayin shugaba yayin da zababben shugaban kasar, Mohamed Bazoum ke hannun sojoji tun bayan juyin mulkin da aka yi a makon jiya, shi ne ya bayyana hakan a wannan Lahadin.

Wannan gargadi dai na zuwa ne bayan da ECOWAS ta bai wa sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar wa’adin kwana bakwai su mayar da hambararren shugaba Mohamed Bazoum kan mulki.

Wannan dai shi ne matakin da kungiyar ta dauka a taron da ta gudanar ranar Lahadi a Abuja, babban birnin Najeriya.

ECOWAS ta yi kira ga hukumomin sojin na Nijar da su gaggauta sakin shugaba Bazoum, tare da mayar da mulki hannun farar hula a kasar.

A sanarwar da babban jami’inta Omar Touray ta fitar, kungiyar ta ce ta yi watsi da takardar ajiye aiki da aka yi ikirarin cewa daga shugaba Bazoum take.

A yayin da ECOWAS ke Allah wadai da ci gaba da tsare Shugaba Bazoum, ta kuma umurci dukkanin hafsan hafsoshin tsaro na kasashe mambobin kungiyar da su ci gaba da gudanar da wani taron gaggawa don tsara dabarun aiwatar da ayyukan soji na maido da tsarin mulki a kasar.

Daga cikin matakan da kungiyar ta dauka akwai rufe kan iyakokin tudu da na sama tsakanin Nijar da mambobin kungiyar tare da haramta wa jiragen sama da suka taso ko suka nufi Nijar ketawa ta sararin samaniyar kasashen kungiyar ECOWAS.

Haka kuma, ECOWAS ta dakatar da huldar kasuwanci da ta kudi tsakanin Nijar da kasashen kungiyar.