Kwamitin Takin Zamani da shugaban kasa ya kafa zai samar da takin zamani buhu miliyan hudu mai nauyin kilo 50 ga manoman kasar nan a kan farashi mai rahusa.
Mai Taimakawa Shugaban Kasa na Musamman Kan Harkokin Yada Labarai da Wayar da Kan jama’a, Malam Garba Shehu ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a jiya.
Sanarwar ta nuna cewa Mataimakin Daraktan a Bangaren Yada Labarai a Fadar Shugaban Kasa, Mista Atta Esah ya ce Shehu ya yi bayanin ne a shirin Hannu Da Yawa na gidan Rediyon Kaduna day a gabata a karshen mako.
Ya ce takin wanda zai iso cikin watan Disamban mai zuwa kari ne a kan buhun taki miliyan shida mai nauyi kilo 50 da tuni aka sayarwa da manoma tun lokacin da shirin ya soma aiki a farkon shekarar nan.