Sabon Gwamnan jihar Bauchi Bala Abdulkadir Mohammed ya bada umarnin gaggawa akan biyan ma’aikatan jihar albashinsu. Maitaimakawa Gwamnan na musamman a fannin yada labarai Mukhtar Mohammed Gidado, ne ya sanar da hakan.
Gwamnan ya bada umarnin ne don rage radadin wahalar da ma’aikatan jihar ke fuskanta.
Za a fara biyan ma’aikatan jihar albashin ne daga yau Juma’a 31 ga Mayu zuwa Litinin 3 ga watan Yuni 2019.