Jam’iyyar APC ta sanar da sakamakon zaben jihar Zamfara inda ta bayyana Alhaji Mukhtar Shehu Idris a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani na neman takarar Gwamna da aka gudanar a jihar Zamfara.
Shugaban jam’iyyar APC na jihar Alhaji Lawali M. Liman ya kuma sanar da Gwamna Abdulaziz Yari a matsayin wanda ya lashe kejerar neman takarar Sanata a shiyyar mazabar Zamfara ta Yamma da kuri’u 166,610.