✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Guinea Bissau ta lallasa Super Eagles

Super Eagles ta koma ta biyu da maki shida.

Tawagar Najeriya ta yi rashin nasara a hannun Guinea Bissau da ci 1-0 a wasan neman shiga Kofin Afirka da suka buga a Abuja, ranar Juma’a.

Wasa ne na uku-uku a rukunin farko don neman gurbin shiga babbar gasar kwallon kafa ta Afirka da za a yi a Ivory Coast a 2024.

Guinea Bissau ta ci kwallon ta hannun Tanguy Zoukrou a minti na 29 da fara wasa a karawar da suka yi a filin wasa na Moshood Abiola a Abuja, Nageria.

Da wannan sakamakon Guinea Bissau ta koma ta daya a rukunin farko da maki bakwai, bayan da ta ci Super Eagles da cin Sao Tome da canjaras da Saliyo.

Super Eagles ta koma ta biyu da maki shida, bayan nasara a kan Saliyo da Sao Tome.

Ranar Laraba Saliyo da Sao Tome suka tashi wasa 2-2 a daya karawa ta uku a rukunin farko.

Ranar Litinin 27 ga watan Maris Super Eagles za ta ziyarci Guinea Bissau, domin buga wasa na hur-hudu a rukunin farko.

Ita kuwa Sao Tome za ta karbi bakuncin Saliyo ranar Lahadi 26 ga watan Maris.