Fashewar gas din girki ya yi sanadiyyar mutuwar mutum takwas dukkan su ‘yan gida daya a cikin garin Dan Musa da ke Karamar Hukumar Dan Musa ta jihar Katsina.
Ga s din ya fashe ne lokacin da ake girki da shi, kuma gobarar ta faru ne da misalin karfe 5 na yamma ranar Asabar lokacin da daya daga cikin wadanda suka rasu take girki a cikin gida.
Rahotan bai tantance sunayen wadanda suka rasu ba, sai makwabtan gidan da abin ya faru sun bayyanawa manema labarai cewa, a cikin wadanda suka rasu akwai matan aure uku da yara biyar.