✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

EFCC ta kama masu POS a Ondo saboda badakalar sabbin kudade

Ana zarginsu da sayar da kudaden a kan farashi mai tsada

Jami’an Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) sun kama gwamman masu sana’ar POS a Jihar Ondo a karshen mako.

An kama mutanen ne saboda zarginsu da badakalar sayar da sabbin kudade a kan farashi mai dan karen tsada.

Aminiya ta gano cewa jami’an hukumar wadanda ke sanye da fararen kaya sun yi wa Akure, babban birnin Jihar kawanya ne a kokarinsu na kama mutanen a manyan kasuwannin birnin.

Bayanai dai sun nuna yawancin mutanen sun rika cin karensu ba babbaka, inda suka rika sayen takardun kudaden daga hannun bankuna suna sayar da su ga mutane a kan farashi mai tsada.

Wani jami’in hukumar da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar wa Aminiya da kamen a wani samame da suka kai Jihar.

Ya ce kai samamen ya biyo bayan wasu bayanan sirri da suka samu ne kan yadda galibin masu sana’ar ke boye sabbin kudaden don kuntata wa jama’a.

Ya ce, “Wani gagarumin samame ne muka gudanar a Akure da wasu sassan Jihar. Mun sami bayanan da ke nuna masu POS na tatsar mutane a kan sabbi da tsofaffin kudi.

“Mun yanke shawarar yi musu dirar mikiya ne musamman a cikin manyan kasuwannin birnin, inda a nan ne wannan dabi’ar ta fi kamari.

“Za mu shafe tsawon mako guda muna wannan aikin, kuma muna yin shi ne domin mu kawo gyara kan yadda kudade za su wadata a Jihar da ma kasa baki daya,” in ji jami’in.