✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

COVID-19: Masu dauke da cutar sun haura 4000 a Najeriya

Wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar coronavirus sun haura mutum 4,000 a Najeriya. Kididdiga ta baya-bayan nan da Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa…

Wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar coronavirus sun haura mutum 4,000 a Najeriya.

Kididdiga ta baya-bayan nan da Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta wallafa sun nuna cewa tsakar daren 9  ga watan Mayu, an tabbatar da karin mutum 239 da suka kamu da cutar, lamarin da ya sanya masu dauke da COVID-19 suka ketara wannan adadi.

Alkaluman na hukumar NCDC dai sun nuna cewa jimilla mutum 4,151 aka tabbatar sun kamu da cutar a Najeriya zuwa yanzu.

Daga cikin wannan adadi kuwa, mutum 128 sun riga mu gidan gaskiya, yayin da aka sallami mutum 745‬ bayan sun warke.

Mutum 97 daga cikin sabbin kamun, kamar yadda alkaluman suka nuna, a jihar Legas suke, 44 a Bauchi, 29 a Kano, 19 a Katsina, 17 a Borno, bakwai  a Yankin Babban Birnin Tarayya.

Sai kuma jihar Kwara mai mutum shida, Oyo mai biyar, Kaduna da Sakkwato na da uku uku.

Biyu a jihohin Ogun, da  Adamawa,‬ da Kebbi‬, sai jihar Ekiti da ke da mutum daya da ya kamu da cutar.