✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

COVID-19: Ba a samu sabbin majinyata ba a Kano

A cikin sa’o’i 24 zuwa karfe 11.55 na daren 16 ga watan Mayu, ba a samu ko mutum guda ba da ya kamu da cutar…

A cikin sa’o’i 24 zuwa karfe 11.55 na daren 16 ga watan Mayu, ba a samu ko mutum guda ba da ya kamu da cutar coronavirus a jihar Kano.

Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano ce ta bayyana hakan a wani sako da ta wallafa a shafinta na Twitter.

Sai dai, a cewar ma’aikatar, an samu “karin mutum biyu da suka riga mu gidan gaskiya yayin da aka sallami mutum uku bayan sun warke”.

Wannan bayani dai ya dace da abin da Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta wallafa, wanda ya nuna babu jihar ta Kano a jerin jihohin da aka samu sabbin majinyata.

A bayanin da NCDC ta wallafa a nata shafin na Twitter dai, a yanzu haka jimillar wadanda aka tabbatar sun kamu da COVID-19 a fadin Najeriya mutum 5,621 ne bayan da aka samu sabbin majinyata 176.

Fiye da rabin sabbin majinyatan dai, wato 95, a jihar Legas suke, yayin da aka samu 31 a jihar Oyo.

Sauran kuwa an same su ne a Yankin Babban Birnin Tarayya (11), da jihohin Neja da Borno (takwas-takwas), da Jigawa (shida), da Kaduna (hudu).

Sai kuma mutum uku a jihar Anambra, bibbiyu a Edo da Ribas da Nasarawa da Bauchi, yayin da Binuwai da Zamfara ke da mutum guda ko wacce.

Zuwa yanzu dai adadin mutanen da suka rasa rayukansu a kasa baki daya ya kai 176; an kuma sallami mutum 1,472 bayan sun warke.