✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Cikin awa 24 an ceto daliban da aka sace a Kogi

Jami’an tsaron hadin gwiwa sun ceto mutane 24, ciki har da dalibai da malamai da ’yan bindiga suka sace a Jihar Kogi, cikin kasa da…

Jami’an tsaron hadin gwiwa sun ceto mutane 24, ciki har da dalibai da malamai da ’yan bindiga suka sace a Jihar Kogi, cikin kasa da awa 24.

A ranar Asabar ne hadin gwiwar ’yan sanda da ’yan banga da sojoji suka ceto mutanen da aka sace su ranar Juma’a, a yankin Adogo na Karamar Hukumar Ajaokuta da ke jihar.

Kakakin ’yan sandan jihar Kogi, William Aya, ya ce akwai dalibai 11 da malamai uku a cikin wadanda aka yi garkuwa da sun da aka kubutar.

Jami’in ya bayyana cewa a yayin musayar wuta a samame da aka kai maboyar ’yan bindigar ne suka tsere suka bar mutanen da ke hannunsu.

Sanarwar da ya fitar ta ce, “A lokacin da rundunar ke sharar dajin domin neman mutanen ne ’yan ta’addan suka hango su daga maboyarsu, suka bude wa tawagar wuta.

“A yayin artabu ne ’yan bindigar suka tsere suka bar mutanen da suka yi garkuwa da su.”