✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Canjin kudi: Emefiele ya yaudari Buhari —Oshiomhole

Ya yi amfani da akidar Buhari ta yaki da rashawa wajen cusa masa ra’ayin sauya takardun kudi.

Tsohon Shugaban jam’iyyar APC na Kasa, Adams Oshiomhole ya ce yaudarar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) Godwin Emefiele ya yi har ya amince da sauyin takardun kudi.

Oshiomhole ya bayyana hakan ne ranar Lahadi a shirin Daily Politic na Gidan Talabijin din Channels.

A cewar Oshiomhole, Gwamnan CBN din ya yi amfani da akidar Shugaban Kasa ta yaki da cin hanci da rashawa wajen cusa masa tsarin.

Shugaban APCn ya kuma ce zargin zagon-kasa da Gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai ya yi a baya-bayan nan kan akwai wasu makusantan Buhari da ke yi wa dan takararsu Bola Tinubu gaskiya ne.

“Babu wata hikima a sauya takardar kudin nan da aka yi.

“CBN yaudarar Buhari ya yi, domin manufarsu shi ne hana gudanar da zaben ma baki daya.

“Kasancewata shugaban jam’iyya, na samu damar yin aiki kai tsaye da Shugaba Buhari, kuma ina mai tabbatar muku da cewa dabara ce Emefiele ya yi wa Shugaban Kasa.

“Na kadu matuka da wannan shirme na CBN, domin ko a zamanin mulkin soja da Buhari ya canja takr6dun kudi, bai hana bankuna bai wa mutane kudi ba, bai kuma takaita musu nawa za su cire ba tunda kudinsu ne,” in ji Oshimhole.

Tsohon Shugaban APCn ya kuma ce: “Ina ganin abin da El-Rufai ke cewa shi ne idan kana ta samun zanga-zanga daga ko’ina a kasa, abinda zai faru shi ne dole ka dakatar da gudanar da zabe saboda babu zaman lafiya.”