✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari ya bukaci ’yan siyasa su yi koyi da Balarabe Musa

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bukaci ’yan siyasa da sauran ’yan kasa sun yi koyi da rayuwar Alhaji Balarabe Musa na rikon gaskiya da amana…

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bukaci ’yan siyasa da sauran ’yan kasa sun yi koyi da rayuwar Alhaji Balarabe Musa na rikon gaskiya da amana da kuma kishin kasa.
A takardar sanarwar da ya sanya wa hannu, Babban Mai Taimakawa Shugaban Kasa Kan Yada Labarai da Wayar da kan Jama’a, Malam Garba Shehu, ya ce Buhari ya yi kiran ne a sakonsa a wurin taron murnar cikar Balarabe Musa shekaru 81 a duniya.
Sanarwar ta nuna cewa Buhari ya kwatanta tsohon gwamnan jihar Kaduna da mutum mai kima wanda ya bar tarihi mai kyau a aikin gwamnati.