✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari ya bukaci Ministocinsa su ci gaba da zama a ofis har ranar rantsuwa

Ranar Litinin mai zuywa dai za a rantsar da Tinubu

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya bukaci Ministocinsa su ci gaba da rike mukamansu har zuwa ranar da za a rantsar da sabon Shugaban Kasa.

A ranar 29 ga watan Mayun 2023 ce Buhari zai mika ragamar mulki ga zababben Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu.

Akwai dai rahotannin da ke cewa Buhari ya sallami Ministocin a yayin taron Majalisar Zartarwa na bankwana da aka gudanar a Fadarsa da ke Abuja ranar Laraba.

To sai dai da yake zantawa da ’yan jaridar Fadar Shugaban Kasa bayan kammala taron, Ministan Yada Labarai da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed, ya ce an umarci dukkan Ministocin su koma su ci gaba da ayyukansu a ma’aikatunsu.

Lai Mohammed ya ce, “Labarin da ake yadawa cewa an rushe Majalisar Ministoci ba gaskiya ba ne. Shugaban Kasa ya umarce mu mu ci gaba da aiki. Saboda haka ba a rushe mu ba, har yanzu muna nan.

“Labarin cewa an rushe mu karya ne. Na tabbatar za mu ci gaba da aiki har nan da ranar 29 ga watan Mayu. Saboda haka ku yi watsi da wancan labarin, ba shi da tushe ballantana makama,” in ji Ministan.