✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Birtaniya ta cire Najeriya a jerin kasashe masu yada COVID-19

Gwamantin Birtaniya za ta janye takunkumin shiga kasarta da ta sanya wa baki daga kasashe 11.

Gwamnatin Biritaniya ta cire sunan Najeriya daga jerin kasashen da ke barazanar yada cutar COVID-19, musamman nau’in Omicron.

Sakataren Lafiya na Birtaniya, Sajid Javid, ya bayyana cewa bullar kwayar cutar Omicron alama ce da ke nuna cewa hana tafiye-tafiye ba zai hana yaduwar sabon nau’in kwayar cutar na COVID-19 ba.

A sakamakon haka, gwamnatin Birtaniya za ta cire Najeriya da sauran kasashen da ta sanya wa bakin daga cikinsu takunkumi daga karfe 4 na yammacin ranar Laraba.

A makon jiya ne gwamantin Birtaniya da sanar da matakin da ta dauka na hana baki daga Najeriya shiga kasarta bayan an samu bullar kwayar cutar Omicron a Najeriya.