✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
  • Trust Radio
  • Trust TV
  • Teen Trust
  • Dailytrust
  • Nigeria Daily
  • Najeriya a Yau
Bincika
Gida - Dailytrust Aminiya
Yi Rajista
  • Gida
  • Labarai
  • Saurari Shirye-Shiryenmu
  • Bidiyo
  • Fagen Siyasa
  • Al'ajabi
  • Dandalin Nishadi
  • Aminyar Kurmi
  • Kasuwanci
  • Wasanni
  • Kasashen Waje
  • ☰
Click Here To Listen To Trust Radio Live
Manyan Labarai

Bankin Afirka: Adesina ya yi tazarce

Dan Najeriya da ya fara zama Shugaban Bankin Raya Afirka ya yi tazarce babu hamayya

Akinwumi Adesina
Shugaban Bankin Afirka, Akinwumi Adesina
    Daga Sagir Kano Saleh
Thu, 27 Aug 2020 11:36:07 GMT+0100

Bankin Raya Kasashen Afirka (AfDB) ya sake zabar tsohon Ministan Gona na Najeriya Akinwumi a Adesina a matsayin shugabansa.

Adesina zai jagoranci bankin a wa’adinsa na biyu na tsawon shekara biyar bayan zaben da aka gudanar a ranar Alhamis, wanda shi ne kadai dan takara.

A ranar Laraba ya bukaci wa’adi na biyu, bayan shafe wata biyar ana kai ruwa rana kan zargin shugabancinsa da gazawa da kuma rashawa a bankin kafin ya wanke shi.

Sau uku sakamakon kwamitocin binciken zarge-zargen na wanke shi, bayan ya sauka daga mukamin domin a yi binciken na karshe wanda wani kwamiti mai zaman kansa ya gudanar.

A jawabin sa ranar Laraba domin neman tazarce wanda babu hamayya ya shaida wa taron shekara na AfDB cewa yana jagorantar bankin ne “domin hidimtawa da kuma sadaukar da kai.”

“Ina yi ne domin hidimta wa Afirka da bankinmu ba tare da wariya ba gwargwadon ikon da Allah Ya ba ni”, inji sanarwar da ya fitar.

Adesina shi ne dan Najeriya na farko da ya taba jagorantar Bankin Raya Afirka, daya daga cikin bankunan duniya guda biyar masu bayar da rance domin ci gaba.

Ana masa kallo a matsayin daya daga cikin manyan wadanda suka taka muhimmiyar rawa wajen habbaka tattalin arziki da ba a saba ganin kamarsu ba.

A watan Oktoban ya samu fice sosai bayan AfDB ya samo gudunmuwar Dala biliyan 115 wanda hakan ya ninka karfin jarin bankin da kuma darajarsa.

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X

Like this:

Like Loading...

Related

  • AfDB
  • Afirka
  • Najeriya
Karin Labarai
  • 2 weeks ago
    ’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki
  • 2 weeks ago
    Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • 2 weeks ago
    Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran - Masana
    An ƙara farashin man fetur a Najeriya
  • 3 weeks ago
    Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • SPONSOR AD

    BIBIYE MU AMINIYA

    • Gida
    • About Us
    • Contact Us
    • Trust +
    • Advertise With Us
    • Privacy Policy
    • Terms of Use
    • Business Directory
    • 20 P.O.W Mafemi Crescent, Utako District, Abuja
    • 700-177-7577
    • [email protected]
    1998 - 2021 Media Trust Limited. All rights reserved.
    %d