✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Bakuwar cuta ta hallaka yara 20 a Afghanistan

Mutane da dama na kwance a cibiyoyin kula da lafiya bayan kamuwarsu da bakuwar cutar

Wata cuta da ba a san irinta ba ta yi sandiyar mutuwar yara 20 a yankin Baghran na kasar Afghanistan.

Daraktan Yada Labarai da Al’adu na Kudancin Lardin Hemand, Hafiz Rashid ya bayyana a ranar Laraba cewa yaran da abin ya shafa sun rasu ne a cikin kwana biyu.

“Muna zargin shan gurbataccen ruwa ne ya haddasa barkewar annobar”, in ji shi.

Yanzu haka dai sauran wadanda suka kamu da cutar suna kwance a asibitocin sha-ka-tafi suna karbar magani.

Rashin ababen more kamar  cibiyoyin lafiya da tsaftataccen ruwan sha na barazana ga rayuwar mutane da dama da suka kamu da cututtuka da za a iya magancewa a yankunan karkara da wurare masu nisa.