✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Babban kalubalen da na fuskanta a shekarun aikina —CP Dikko

Ya kamata Gwamnatin Kano da kotuna jihar su shawo kan wannan matsala.

Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano mai barin gado, CP Sama’ila Shu’aibu Dikko, ya ce babban kalubalen da ya fuskanta a Kano shi ne yadda ake bayar da belin wadanda suka aikata manyan laifuka bayan an kai su kotu.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a jawabinsa na bankwana a hedikwatar rundunar da ke Bompai.

A ranar Laraba ne dai Kwamishinan zai yi ritaya daga aiki, sakamakon cikarsa shekaru 60 da haihuwa.

CP Dikko ya fara aiki a matsayin Kwamishinan ‘yan Sanda daga ranar 19 ga watan Fabrairun 2019.

CP Dikko ya kirayi Gwamnatin Kano da Kotuna a jihar da su duba yiwuwar aiwatar da abinda ya dace dangane da wannan kalubale na bayar da belin wadanda ake zargi da aikata manyan laifuka.

A cewarsa, “bai kamata a ce wani ya aikata babban laifi ba, kuma a sha wahalar kamo shi amma ya fi karfin doka ba.

Kazalika, CPn ya yi kira ga sauran jami’an rundunar, da su kasance masu bin dokar aikin na dan sanda a duk inda suka tsinci kansu.

Ana iya tuna cewa, a kwanan baya an samu dambarwa a Kano lokacin da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yafe wa wasu mutane da aka kama bisa zarginsu da tayar da hankulan jama’a.