✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ba za mu yi zaben a mutu ko a yi rai ba –Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce, bai kamata ‘yan siyasan Najeriya su dauki zaben 2019 a matsayin zaben a mutu ko a yi rai ba.…

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce, bai kamata ‘yan siyasan Najeriya su dauki zaben 2019 a matsayin zaben a mutu ko a yi rai ba.

Shugaban ya bayyana hakan ne a sakon sabuwar shekara ga ‘yan Najeriya, Shugaba Buhari wanda ke neman wa’adi na biyu a zaben ranar 16 ga Faburairu 2019, wanda za a yi zaben ‘yan takarar shugaban kasa da na majalisar dattawa ya bukaci ‘yan Najeriya su gudanar da sahihin zabe.