Sanata Suleiman Asonya Adokwe ya ce ya ajiye siyasa. Hakan na zuwa ne bayan tsohon Sanatan na Nasarawa ya gaza karbe kujerarsa a kotun karar zabe. Sanata Suleiman Adokwe ya wakilci Nasarawa ta Kudu a Majalisar Dattawa a karkashin Jam’iyyar PDP. Tsohon Gwamnan Jihar, Sanata Umaru Tanko Al-Makura ne ya samu nasara a kansa a zaben da aka gudanar a bana.
Adokwe ya ce “A shekaruna yanzu a duniya ba zan iya zuwa ina neman kujerar siyasa ba. Na kai matsayin da zan zama dattijo, amma tsayawa takara ba ya cikin lissafina a yanzu.” Sanatan ya nuna cewa ya amince da shari’ar da kotun ta yi inda aka tabbatar da nasarar Sanata Umaru Tanko Al-Makura a matsayin Sanatan Kudancin Nasarawa.
Sanata Adokwe ya bayyana cewa bai da ja da zabin da UbangijiYa yi a shari’ar da ya daukaka, ganin cewa ya yi aiki a Majalisar Dattawa na shekara 12.
Sau uku ana zaben Sanata Adokwe a matsayin dan Majalisar Dattawa. Sai dai a wannan karo ne ya sha kaye a hannun tsohon Gwamna Umar Tanko Al-Makura na Jam’iyyar APC. Tsohon Sanatan na Nasarawa ta Kudu ya shigar da kara a kotu yana kalubalantar nasarar da APC ta samu. Sanatan bai yi nasara ba, don haka ya daukaka kara, inda a nan ma aka ba APC gaskiya.