Shugaban Kungiyar Masu Shirya Fina-Finan Hausa (MOPPAN), Alhaji Kabiru Mai Kaba ya ce ba su yarda da matakin da Hukumar Tace Fina-Finai ta dauka kan yafewa Rahama Sadau ba.
Kabiru Maikaba ya yi wannan bayanin ne bayan Shugaban Hukumar Tace-Tacen, Isam’ila Afakallah ya yi jawabin cewa sun yafewa jarumar, sannan kuma a shirye suke su ci gaba da tace fina-finan da ta fito a ciki, ko kuma ta xauki nauyi.