✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Auren wuri na ‘kashe’ mata 60 kullum a Najeriya

Mata 22,000 ke mutuwa duk shekara a wajen matsalolin daukan ciki ko haihuwa.

Kungiyar Kare Hakkin Bil Adama ta Save the Children, ta ce auren wuri na sanadin rayuwar fiye da mata 60 kullum a Najeriya.

Save the Children ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar a daren Litinin yayin bikin ranar ’ya’ya mata ta duniya.

Kungiyar a rahotanta, ta ce kashi 44 cikin 100 na ’ya’ya mata a Najeriya ana musu aure kafin su cika shekaru 18 a duniya, wanda wannan shi ne adadi mafi yawa a duniya.

Save the Children cikin sanarwar da shugabarta, Inger Ashing ta sanya wa hannu, ta ce mata a Najeriya na rayuwa mafi wahala a duniya.

Ta kuma shaida cewa mata 22,000 ke mutuwa a kowace shekara a wajen matsalolin daukan ciki ko haihuwa.

Cikin sabbin alkaluman da Kungiyar ta fitar, ta ce a Yammacin Afirka da kuma Afirka ta Tsakiya, ana samun kusan rabin matan da ke mutuwa saboda auren wuri da aka kiyasta a fadin duniya.