Jam’iyya mai mulki ta APC ta shirya tsaf don karbar tsohon shugaban jam’iyyar adawa ta PDP kuma tsohon Gwamnan Bauchi Ahmadu Adamu Mu’azu.
Wannan yazo daidai ne da lokacin da jam’iyyar PDP ta dakatar da wasu jigogin jam’iyyar ciki harda mataimakinta shugaban jam’iyyar Sanata Babayo Garba Gamawa da Alhaji Kaulaha Aliyu inda suka fice daga jam’iyyar.
Ana saran Shugaba Buhari ne zai karbi Adamu Mu’azu zuwa jam’iyyar APC a gangamin yakin neman takarar shugaban kasa da zai zo jihar.