Wani ne ya yi aure amma bai daina fitsarin kwance ba. Rannan ya kwanta barci sai ya yi fitsarin kuwa. Da ya tada matarsa sai yake tambayarta cewa: “Idan ke ce kika yi mafarkin kura da zaki da damisa sun biyo ki a cikin tsakiyar daji, yaya za ki yi?” Sai ta ce masa: “Tabdijam! Ai sai na yi zawayi!” Sai ango ya ce: “Lallai ashe ni jarumi ne, ni fitsari kawai na yi!
Daga Mudassir Ibrahim Mando, 08024122559